Da dumi-dumi: Majalisar Dokokin jihar kano zata gayyaci Dan adaidaita sahu da ya tsinci Miliyan 15

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

 

Majalisar Dokokin jihar kano ta amince zata gayyato matashin dan adaidaita sahu nan da ya tsinci Naira Miliyan 15 kuma ya mayarwa Mai shi.

 

Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Doguwa, Hon. Salisu Ibrahim Muhammad, ne yayi kira ga majalisar da ta gayyaci Salisu Auwalu wanda ya tsinci kudi kimanin naira miliyan 15 domin a karramashi a majalisar.

Talla

Shugaban majalisar, Jibril Ismail Falgore, yace zasu gayyaci matashin, kuma za suyi masa karo-karo cikin albashin su.

 

Yayin zaman majalisar, dan majalisa Muhammad ya ce matashin ya nuna tsantsar tawakkali da kuma hali na gari wajen mayar da kudaden idan aka yi la’akari da halin matsin da ake ciki, a don haka ya kamata majalisar ta karrama shi.

Da dumi-dumi: Kotu ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan jihar Zamfara

Wannan ce ta sa shugaban majalisar ya amince da bukatar, yayin da ya amince a gayyaci matashin sannan yayi alkawarin cewa majalisar zata tallafa masa.

Yanzu-Yanzu: Tinubu Yayi Sabbin Nade-nade a ofishin mataimakin Shugaban kasa

Tun da Salisu ya mayar da wadancan kudade al’umma da dama suka yi yaba masa tari da yi masa kyaututtuka kala-kala domin Kara masa kwarin gwiwar cigaba da zama mai amana.

Yanzu haka ma mun sami labarin mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya baiwa mahaifin matashin kyautar kayan abinci da da tufafi, domin karama musu kwarin gwiwar cigaba da yiwa ya’yansu tarbiyya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...