Da dumi-dumi: Kotu ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan jihar Zamfara

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Zamfara ta kori karar da jam’iyyar APC ta shigar, ta kuma tabbatar da nasarar Dauda Lawan, a matsayin halastaccen zababban Gwamnan jihar Zamfara.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito bayan da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana Dauda Lawan na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar, hakan tasa Bello Muhammad Matawalle na jam’iyyar APC ya shigar da kara Inda yake ƙalubalantar nasarar da Dauda Lawan ya samu a gaban kotu.

Talla

 

A zaman yanke hukunci da kotun ta yi yau a birnin Sokoto, ta ce Dauda shi ne ya samu ƙuri’u mafi yawa a zaɓen.

 

Tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle ne ya shigar da ƙara yana ƙalubalantar nasarar Dauda a kotun wadda ke zaman ta a birnin Sokoto.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...