Da dumi-dumi: Kotu ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan jihar Zamfara

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Zamfara ta kori karar da jam’iyyar APC ta shigar, ta kuma tabbatar da nasarar Dauda Lawan, a matsayin halastaccen zababban Gwamnan jihar Zamfara.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito bayan da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana Dauda Lawan na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar, hakan tasa Bello Muhammad Matawalle na jam’iyyar APC ya shigar da kara Inda yake ƙalubalantar nasarar da Dauda Lawan ya samu a gaban kotu.

Talla

 

A zaman yanke hukunci da kotun ta yi yau a birnin Sokoto, ta ce Dauda shi ne ya samu ƙuri’u mafi yawa a zaɓen.

 

Tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle ne ya shigar da ƙara yana ƙalubalantar nasarar Dauda a kotun wadda ke zaman ta a birnin Sokoto.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...