Yanzu-Yanzu: Tinubu ya sake nada sabbin ministoci guda 2

Date:

 

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da nadin Dr. Jamila Bio Ibrahim a matsayin ministar matasa, har zuwa lokacin da majalisar dattawan tarayyar Najeriya ta amince da ita.

 

Shugaban ya kara amincewa da nadin Mista Ayodele Olawande a matsayin karamin ministan matasa, har zuwa lokacin da majalisar dattawan tarayyar Najeriya ta amince da shi.

Talla

Kadaura24 ta rawaito Hakan dain na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban kasa Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Zamu samar da ingantacceen tsarin samar da gidaje ga yan Nigeria – ATM Gwarzo

Dokta Jamila Bio Ibrahim matashiyar likita ce kuma a baya-bayan nan ta taba rike mukamin shugabar kungiyar Matasa ta (PYWF). Ta kuma yi aiki a matsayin babbar mataimakiya ta musamman ga gwamnan jihar Kwara kan maradun ci gaba mai dorewa (SDGs).

Shi kuwa Mista Ayodele Olawande kwararre ne wajen sha’anin ciyar da al’umma kuma shugaban matasa a jam’iyyar APC mai mulki. Kwanan nan ya yi aiki a ofishin mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan kirkire-kirkire daga 2019 zuwa 2023.

Shugaba Tinubu ya bukaci wadanda aka nadan da su tabbatar da cewa suna nuna kwazo da kuma kawo cigaba ga matasan Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...