Yanzu-Yanzu: Tinubu ya sake nada sabbin ministoci guda 2

Date:

 

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da nadin Dr. Jamila Bio Ibrahim a matsayin ministar matasa, har zuwa lokacin da majalisar dattawan tarayyar Najeriya ta amince da ita.

 

Shugaban ya kara amincewa da nadin Mista Ayodele Olawande a matsayin karamin ministan matasa, har zuwa lokacin da majalisar dattawan tarayyar Najeriya ta amince da shi.

Talla

Kadaura24 ta rawaito Hakan dain na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban kasa Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai.

Zamu samar da ingantacceen tsarin samar da gidaje ga yan Nigeria – ATM Gwarzo

Dokta Jamila Bio Ibrahim matashiyar likita ce kuma a baya-bayan nan ta taba rike mukamin shugabar kungiyar Matasa ta (PYWF). Ta kuma yi aiki a matsayin babbar mataimakiya ta musamman ga gwamnan jihar Kwara kan maradun ci gaba mai dorewa (SDGs).

Shi kuwa Mista Ayodele Olawande kwararre ne wajen sha’anin ciyar da al’umma kuma shugaban matasa a jam’iyyar APC mai mulki. Kwanan nan ya yi aiki a ofishin mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan kirkire-kirkire daga 2019 zuwa 2023.

Shugaba Tinubu ya bukaci wadanda aka nadan da su tabbatar da cewa suna nuna kwazo da kuma kawo cigaba ga matasan Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...