Kamfanin Simintin Dangote ya ɗauki nauyin koyawa matasa sana’ar kiwon kaji

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

A kokarin cike gibi a harkar kiwon kaji da kasuwanci a Nigeria, Kamfanin Simintin Dangote ya fara koyawa Matasa sana’ar kiwon kaji .

Janar Manaja Mai kula da harkokin al’umma da aiyuka na musamman na kamfanin Mista Ademola Adeyemi, aikin wani bangare ne na shirin wayar da kan al’umma na shekarar 2023 ga matasa a cikin al’ummomin jihar Kogi.

Talla

Ya ce shiga tsakanin zai taimaka wa gwamnati wajen bunkasa harkokin kiwon kaji da kasuwancinsa

A cewarsa, kawo yanzu an dauki matasa 30 da aka zabo daga yankuna daban-daban.

Daliban Firamare Sama da Miliyan 5 Ake Da su a Kano, Miliyan 4 Daga Cikin su a Kasa Suke Zama

Mista Adeyemi ya ce al’ummomin da suka ci gajiyar shirin sun fito ne daga Oyo, Obajana, Iwaa da Apata.

“Ana sa ran horon zai taimaka wajen bunkasa samar da kaji, sarrafawa, da kuma samar da su,” in ji shi.

Al-ameen G-Fresh da Sadiya Haruna sun bayyana makomar Aurensu

A cewarsa, an mika wa wadanda suka ci gajiyar wannan bukin na Starter a wani taron da ya samu halartar manyan masu ruwa da tsaki.

Abubuwan da ke cikin fakitin, in ji shi, sun haɗa da: Wurin Kwanciyar Kaji, Cajin Baturi, Magungunan Ciyar da sauran kayan aikin aiki.

Ya ce Kwalejin Ilimi ta Kabba ita aka dorawa alhakin gudanar da horon a madadin kamfanin na Dangote.

Shugaban kwalejin, Dr. Jagboro Victoria Olusola (Mrs.) ya yabawa kamfanin simintin Dangote bisa wannan shiri na inganta rayuwar al’umma .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...

Ana daf da yin jana’izar Aminu Dantata a Madina

Tawagar da gwamnatin Najeriya ta tura zuwa Madina na...

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...