Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya Baiwa Kwamishinonisa Sabon Umarni

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta umarci jami’anta wadanda suka haɗar da kwamishinoni da masu baiwa gwamna shawara da dukkanin wani mai mukami a gwamnatin da ya guji yin kalaman da basu da nasaba da hukuma ko ma’aikatarsu.

 

Kwamishinan ma’aikatar yada labarai da harkokin cikin gida na jihar kano Baba Halilu Dantiye ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai ya gudanar a gidan gwamnatin kano.

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano ya Kori kwamishinan kasa da mai bashi shawara kan harkokin Matasa

Kwamishinan yace Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya umarci dukkanin masu rike da mukamai a gwamnatinsa da su tabbatar duk maganar da zasu yi musamman a kafafen yada labarai tana da nasa ba da ma’aikatun da suke jagoranta .

” Idan harkar ma’aikatarka ce kana da dama kayi magana akai saboda kafi kowa saninta , Amma idan ba haka to sai ka nemi izini Kuma sai ka jira har an baka dama sannan sai ka yi”. Inji Baba Dantiye

Talla

Yace Kuma gwamnan ya jaddada cewa gwamnatin jihar kano bata sake lamuntar wani jami’inta ya yi kalamai na tunzura al’umma ba, Inda yace gwamnatin zata ɗauki matakin da ya dace akan duk wanda ya sabawa wanann umarni.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a jiya gwamnan kano Abba Kabir Yusuf ya sallami kwamishinan kasa da safayo na jihar Adamu Aliyu Kibiya da mai bashi shawara kan harkokin Matasa da wasanni Yusuf Imam Wanda aka fi sani da Ogan Boye daga kan mukamansu, saboda kalaman tunzura al’umma al’umma da kuma barazanar kashe alkarai da sukai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...