Bayan na yiwa Atiku ritaya zan Saya Masa Akuyoyi ya cigaba da kiwo – Kashim Shettima

Date:

Daga Hafsat Yusuf Sulaiman

 

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya ce zai yiwa dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023 Alhaji Atiku Abubakar ritaya r siyasa kuma ya saya masa dabbobi don ya je yayi kiwonsu.

 

Shettima ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan da kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa ta tabbatar da nasarar da shugaba Bola Tinubu ya samu a kotun daukaka kara a ranar Laraba.

Talla

Bayan ya bayyana gamsuwarsa da hukuncin kotun da kuma yin kira ga abokan adawa da su hada kai da su, daya daga cikin ‘yan jarida ya tambaye shi ko har yanzu zai yi ritaya Atiku – daya daga cikin kalamansa a lokacin yakin neman zabe.

Da dumi-dumi: Bayan korar karar Atiku, Kotun ta tabbatar da nasarar Tinubu

Tsohon gwamnan jihar Borno ya ce, “Mun wuce matakin siyasa. Yanzu, muna cikin al’amuran mulki ne, Atiku Abubakar dattijo ne wanda nake matukar girmama shi.

“Duk wanda ya san yadda ake mu’amala da al’adu tsakanin Fulani da Kanuri a arewa, zai san cewa ina da ‘yancin yi masa wasa, kuma ya hakura.

“Ba za mu yi wa Atiku ritaya zuwa Dubai ko Morocco ba, zan yi masa ritaya ne zuwa Fombina. kuma zan sayo masa akuyoyi da kaji domin yaje ya cigaba da kiwonsu.

Talla

“A magana ta gaskiya Atiku dattijo ne da al’umma suke bukatarsa.

“Kwarewa ba abu bace da za ku iya saya a kasuwa ba. Mun amfana kwarai da tarin kwarewarsa da gogewarsa. Amma yanzu ya kamata ku sani yanzu lokacin siyasa ya wuce lokaci ne da zamu maida hankali wajen hidimtawa al’umma .”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...