Majalisar tarayya:Kotun sauraron kararrakin zabe a kano ta Kori karar dan takarar APC a Kiru da Bebeji

Date:

Daga Zakariyya Adam Jigirya

 

Kotun sauraren kararrakin zabe ta Majalisar Dokoki a jihar Kano da ke ta ce AMuhammad Sanusi Said kiru na APC ya gaza wajen gabatar da hujjoji don tabbatar da cewa ba a yi sahihin zaben dan majalisar tarayya ba a kananan hukumomin Kiru/Bebeji, wanda ya baiwa Abdulmumini Jibrin Kofa na NNPP nasara.

Talla
Talla

Jagorar alkalan guda uku Mai Shari’a Ngozi Flora ta bayyana cewa takardun da bangarorin biyu suka gabatar a gaban kotun sun nuna cewa Abdulmumini Jibrin Kofa ya ajiye mukaminsa na Babban Sakataren Hukumar Gidajen Tarayya, kwanaki 30 gabanin gudanar da zaben da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu 2023 a sabanin da’awar mai kara.

Mai shigar da kara ya kasa baiwa Kotun hujjojin cewa an tafka kura-kurai a zaben dan majalisar tarayya na Kiru da Bebeji ba, Inda yace ba’a bin dokar zabe ta 2022 ba a zaben.

Saboda haka mun kori wannan karar saboda rashin gamsassun hujjoji.

Talla

Kotun ta yi umarci wanda yayi kara da ya biya wanda akai Kara Kuɗin N100,000 .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...