NAFDAC ta yi Allah-wadai da masu amfani da wani sinadari wajen nunar da ‘ya’yan itatuwa

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) a ranar Litinin ta yi Allah wadai da amfani da sinadarin calcium carbide wajen saurin nunar da ‘ya’yan itatuwa.

 

Babbar daraktar hukumar ta NAFDAC, Farfesa Mojisola Christianah Adeyeye, ta yi Allah-wadai da lokacin kaddamar yayin bitar da NAFDAC ta shiryawa yan jaridu kan illolin da ke tattare da fataucin miyagun kwayoyi da kuma amfani da sinadarin Calcium Carbide wajen nika ‘ya’yan itatuwa wanda aka gudanar a garin Lafia na jihar Nasarawa.

Talla

“Akwai kiraye-kirayen da ‘yan Najeriya masu hankali suka yi kan bukatar daukar tsauraran matakai don dakile bala’in safarar miyagun kwayoyi da amfani da sinadarin calcium carbide wajen nika ‘ya’yan itatuwa.

Da dumi-dumi: Kotun Sauraren Kararrakin Zaben Shugaban Kasa ta Bayyana Ranar da Zata Yanke Hukunci

“Bugu da kari, jaridu da dama a Nigeria da kungiyoyi masu zaman kansu sun nuna damuwa game da hadarin da ke kunno kai da hatsarin da za’a iya fadawa wadannan munanan ayyuka guda biyu da wasu marasa kishin kasa suke yi a Nigeria kawai saboda su sami kudi,” in ji ta.

Shugaban hukumar wanda ya samu wakilcin daraktan tantance sinadarai da bincike na hukumar, Dr Leonard Omokpariola, ya bayyana cewa, kaddamar da taron bitar wayar da kan ga yan jaridu, cika alkawarine da hukumar su ta yi na ci gaba da karfafa hadin gwiwar NAFDAC da kungiyar ‘yan jarida masu bada rahoton lafiya a Najeriya, wajen hada kai. ilimantarwa da wayar da kan ‘yan jaridun Najeriya da kuma wayar da kan ‘yan jaridun su taka rawar gani a kokarin da ake yi na kawar da matsalar fataucin miyagun kwayoyi da sanar da mutane Illar amfani da sinadarin Carbide wajen nunar da ‘ya’yan itatuwa ga lafiyar al’ummar Nigeria.

Talla

Adeyeye ya kara da cewa, barazanar safarar miyagun kwayoyi kalubale ne babba ga tsarin samar da kiwon lafiya a kasar wanda hakan zai tabbatar da kudurin hukumar NAFDAC na hana sayar da kwayoyi da sinadarin da suke cutar lafiyar al’umma .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...