Daga Rahama Umar Kwaru
Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta ce ta gano shirin da wasu mutane ke yi na gudanar da zanga-zangar tashin hankali a faɗin ƙasa domin nuna gazawar gwamnatin tarayya da kuma jami’an tsaro na magance batun matsin rayuwa da mutane ke ciki.

DSS ta ce tana sanya ido kan shugabannin kungiyoyin domin dakatar da su daga jefa ƙasar cikin zaman rashin doka.
Da dumi-dumi: Kotun Sauraren Kararrakin Zaben Shugaban Kasa ta Bayyana Ranar da Zata Yanke Hukunci
Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun DSS ɗin Peter Afunanya ya fitar, ta ce an samu bayanan sirri da ke nuna cewa mutane da ke shirin yin zanga-zangar sun kunshi wasu ƴan siyasa da ke haɗa kan shugabannin ɗailbai, kungiyoyin kabilu da matasa da kuma fusatattun kungiyoyi.
NNPP za ta binciki Kwankwaso da wasu kan zargin karkatar da kudin takarar N1b
Hukumar ta kuma shawarci shugabannin Jami’o’i da sauran makarantu da su ja hankalin ɗalibansu daga shiga cikin abubuwan da za su janyo rashin zaman lafiya.

Har ila yau, DSS ɗin ta buƙaci iyaye da su riƙa yi wa ‘ya’yansu nasiha na su guji shiga cikin abin da zai karya doka da oda.
Hukumar ta sha alwashin kama duk wanda ya yi ƙoƙarin tayar da zaune tsaye a faɗin ƙasar.