Juyin Mulki: Sojojin Nijar zasu gurfanar da Muhd Bazoum bisa laifin cin amanar kasa

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta sha alwashin gurfanar da hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum a gaban kuliya saboda “cin amanar kasa” tare da yin silar shugabannin kasashen Afirka ta Yamma suka kakabawa kasar takunkumi.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito, Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ta ECOWAS ta kakabawa Nijar takunkumai, sakamakon juyin mulkin da aka yi, kuma ba ta yanke hukuncin yin amfani da karfi ba, kan sojojin da suka hambarar da gwamnatin Dimokaradiyya ta Bazoum a ranar 26 ga watan Yuli ba.

Talla

Kungiyar ECOWAS dai ta amince da aikewa da dakarun sojojin don a shirin ta na ko ta kwana don mayar da amfani da kundin tsarin mulkin Jamhuriyar Nijar cikin gaggawa amma duk da haka Kungiyar tana ta ci gaba da kokarin ganin an warware rikicin ta hanyar diflomasiyya.

Dalilai Guda 10 da DSS ta bayar kin Amincewa da El-Rufai a matsayin Ministan Tinubu

Shugabannin mulkin sojin Nijar sun ce za su tuhumi Bazoum da laifin cin amanar kasa da kuma kawo cikas ga tsaron ciki da wajen Nijar, a cewar wata sanarwa da Kanar-Major Amadou Abdramane ya karanta a gidan talabijin na kasar.

Sojoji Ba Su Taba Samun Buƙatar yin Juyin Mulki a Nigeria ba – Hedikwatar tsaro

Bazoum, mai shekaru 63, da iyalansa suna tsare a gidan shugaban kasar na Yamai tun bayan juyin mulkin, tare da nuna damuwar kasashen duniya kan yanayin da yake ciki.

” Tiani ya ce Kofar su a bude take don samun masalaha ta hanyar diflomasiyya da zaman lafiya wajen warware matsalar”, in ji Sheikh Bala Lau, kwana guda bayan tawagar malaman addinin musulunci na Najeriya sukai da shi a babban birnin Yamai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa magwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...