Maryam Shetty ta Magantu kan Cire Sunanta daga Cikin Ministocin Tinubu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Matashiyar nan wadda shugaban kasa Bola Tinubu ya sanya sunanta cikin ministocinsa Maryam Shetty ta bayyana Rashin damu bisa yadda Shugaban kasa ya cire sunanta daga cikin ministocinsa.

 

” Yayin zaman majalisa a wannan rana ta juma’ar nan, na sami labarin cire sunana daga cikin wadanda Shugaban kasa Bola Tinubu zai nada a matsayin ministocinsa, tare da maye gurbina da Dr. Mahmoud Mairiga”. Inji Maryam Shetty

Talla

Maryam Shetty ta bayyana hakan ne a sashin shafinta na Twitter, jim kadan bayan sanar da cire sunanta daga cikin ministocin.

Yanzu-Yanzu: Tinubu ya sauya sunan Maryam Shetty daga Ministocinsa

” Ina matukar jin dadin da godiya da matakin da shugaban kasa ya dauka”. Inji Shetty

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa a zaman majalisar dattawa ta wannan rana ta juma’a Shugaban kasa Bola Tinubu ya aikewa majalisar da wasikar sauya sunan Maryam Shetty da Mariya Mahmoud Bunkure, bayan tura sunan a ranar laraba mai zuwa.

 

Har yanzu dai babu sashihin labarin dalilin da yasa aka sauya sunan Maryam Shetty daga cikin ministocin da Shugaba Tinubu zai nada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Aminu Dantata: Duniyar Kasuwanci ta yi Babban Rashi – Shugaban Kamfanonin Gerawa

Shugaban rukunonin Gerawa group of Companies Dr. Ibrahim Muhammad...

Da dumi-dumi: Wasu kungiyoyin APC a Kano sun fara kiraye-kirayen Abdullahi Abbas ya sauka daga shugaban jam’iyyar

Daga Hafsat Abdullahi Muhammad Kungiyoyin jam'iyyar APC da suka hadar...

Bayan Amincewar Kasar Saudia , an Sanya Ranar Binne Aminu Dantata a Madina

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid...

Rashin Alhaji Aminu Dantata Babban Rashi ne ga harkokin kasuwanci a Duniya – Salbas

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Babban kamfani a masana'antar mai a...