Kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC a Najeriya ya tabbatar da zaɓen Dakta Abdullahi Umar Ganduje, tsohon gwamnan jihar Kano, a matsayin sabon shugaban riƙo na jam’iyyar.
Shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu na cikin manyan ƙusoshin jam’iyyar da suka halarci taron kwamitin zartarwar APC na ranar Alhamis.

An zaɓi Ganduje ne a lokacin taron kwamitin gudanarwar jam’iyyar na 12 da aka gudanar a otal ɗin Transcorp Hilton da ke Abuja babban birnin ƙasar.
Cikakkun sunayen ministocin Tinubu guda 47 da Jihohin su
Tun da musalin karfe 9:30 ne mambobin kwamitin suka fara halartar ɗakin taron da ke otal din Transcorp Hilton, da ke Abuja babban birnin ƙasar.
Ranar 17 ga watan Yuli Shugaban jam’iyar na ƙasar sanata Abdullahi Adamu da babban sakaraten jam’iyyar Sanata Iyiola Omisore suka sanar da ajiye muƙamansu na shugabancin jam’iyar.
Inda jam’iyyar ta sanar da naɗin Sanata Abubakar Kyari, wanda shi ne mataimakin shugaban jam’iyyar shiyyar arewacin ƙasar, a matsayin shugaban riƙo na jam’iyyar.
To sai dai a ranar 27 ga watan Yuli ne shugaban ƙasar Bola Tinubu ya sanya sunan Sanata Abubakar Kyari cikin jerin sunayen da ya aika Majalisar Dattawan ƙasar don tantance su a matsayin ministocin gwamnatinsa.
Tun bayan saukar Abdullahi Adamu ne ake ta raɗe-raɗin cewar Abdullahi Ganduje ne zai maye gurbinsa a matsayin sabon shugaban riko na jam’iyyar.
Gabanin hakan dai ana ta ce-ce-ku-ce kan ko sunan tsohon gwamnan na Kano, kuma ɗaya daga cikin manyan na-hannun daman shugaban ƙasar, yana cikin waɗanda Tinubun zai bai wa muƙamin minista, musamman saboda rawar da ya taka tun farko wajen samun nasarar shugaban ƙasar a zaɓen 2023.