Matatar Mai Ta Fatakwal Za Ta Fara Aiki a Watan Disamba -Tinubu

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Shugaban Nigeria Bola Tinubu ya tabbatar wa shugabannin kungiyar kwadago cewa matatar mai ta Fatakwal za ta fara aiki nan da watan Disamba na Shekarar 2023.

 

Kungiyar kwadagon ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a daren Laraba, a Abuja bayan wata ganawa da suka yi da shugaba Bola Tinubu.

Talla

Shugabannin kwadagon sun kuma bayyana cewa, shugaban ya yi alkawura da dama inda suka amince da komawa kan teburin tattaunawa.

Cikakkun sunayen ministocin Tinubu guda 47 da Jihohin su

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da shugabannin kungiyar kwadago ta Najeriya, Joe Ajaero da Trade Union Congress, Festus Osifo suka fitar.

Sanarwar ta kuma yabawa ‘yan Najeriya bisa goyon bayan zanga-zangar da suka yi a fadin kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...