Juyin Mulki: Abdulsalami Abubakar, da Sarkin Musulmin Nigeria sun dira a Jamhuriyar Nijar

Date:

Daga Maryam Ibrahim Abubakar

 

Wakilan kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) tsohon shugaban kasa Nigeria Janar Abdussalam Abubakar mai ritaya da mai alfarma Sarkin Musulmin Nigeria Muhammadu Sa’ad Abubakar sun isa birnin Yamai na Jamhoriyyar Nijar fadar mulkin kasar.

 

Wakilan kungiyar ta ECOWAS sun je kasar Nijar din ne domin lalubo bakin zaren yadda za’a warware rigingimun da ke faruwa a kasar, biyo bayan juyin mulkin da sojoji suka yi na hambarar da zababbiyar gwamnatin dimokuradiyya kwanaki kadan da suka wuce.

Talla

Ana sa ran manyan ‘yan Najeriyan biyu za su tattauna da shugabannin da suka yi juyin mulki a Kasar ta Nijar.

Abubuwan da ya kamata ku sani game da Sabon Ministan da Tinubu zai nada daga Kano Engr. Abdullahi T Gwarzo

Wata sanarwa mai dauke da sa hannun Ajuri Ngelale – mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai ranar Alhamis, ta ce Tinubu ya aike da wakilai zuwa Yamai, kuma ya bukaci tattaunawa mai karfi don kawo karshen matsalar.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a makon da ya gabata ne sojojin Kasar Nijar suka hambarar da gwamnatin farar hula ta ƙasar wadda ke karkashin jagorancin Shugaban kasa Muhammad Bazoum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...