Gwamnatin Kano ta bayyana dalilin tantace ma’aikatan REMASAB

Date:

Daga Kamal Umar Kurna

 

Gwamnatin jihar Kano tace ta kaddamar da aikin tantance ma’aikatan hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli ta jihar, ne domin gano bara gurbi da gano matsalolin wasu daga cikin ma’aikatan suke fuskanta domin inganta ayyukansu.

 

Kwamishinan Ma’aikatar Muhalli ta jihar Kano Honourable Nasiru Sule Garo ne ya bayyana hakan lokacin da yake kaddanar da aikin tantance ma’aikatan a hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli ta jihar nan.

Talla

Garo yace duba da yadda koke suka yi yawa daga cikin ma’aikatan hukumar musamman kanana ma’aikatarsa, hakan yasa gwamnati taga dacewar tantance ma’aikatan tare da yin garanbawul domin samun cikakkiyar nasarar ayyukan Ma’aikatar.

Da dumi-dumi: Muhimman gabobi 5 na Jawabin Shugaban Tinubu

Da yake jawabi tun da farko tsohon shugaban hukumar kwashe shara ta jihar Kano Injiniya Abdullahi Shehu Wanda shine shugaban kwamitin tantance ma’aikatan, ya bukaci hadin kan ‘yan kwamitin nasa domin gudanar da aikin cikin nasara.

Daga karshe kwamishinan Ma’aikatar Muhallin ta jihar Honourable Nasiru Sule Garo yace kwamitin zai yi aikinsa cikin kwanaki 5 tare da Mika rahotonsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...