Wata Kotu a Kano ta tsare wani mutum da ya kira abokinsa dan luwadi

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

A ranar Alhamis ne wata kotun shari’ar Musulunci a jihar Kano ta bayar da umarnin tsare wani matashi dan shekara 25, Aliyu Sa’ad, wanda ya amsa laifin kiran abokinsa dan luwadi, a gidan gyaran hali.

 

Alkalin kotun, Malam Umar Lawal-Abubakar, ya bayar da umarnin ne biyo bayan amsa laifin da Sa’ad ya shigar.

Za mu samar da sabbin wuraren kasuwanci a Kano don rage cunkoso a birnin jihar – Abba Gida-gida

Lawal-Abubakar ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 3 ga watan Yuli domin ci gaba da shari’ar.

 

Tun da farko, Lauyan masu shigar da kara, Insp Abdullahi Wada, ya shaida wa kotun cewa wanda ake kara ya aikata laifin ne a ranar Litinin da misalin karfe 8 na dare.

Tallah

Wada ya kuma ce wanda ake kara ya kira wanda yake kara, Malam Ahmed Khamis-Ahmed da sunan da bai dace ba bayan wata hatsaniya da sukai.

 

Mai gabatar da kara ya ce laifin ya ci karo da tanadin sashe na 188 na shari’ar Musulunci ta jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...