Kotu ta mayar da Mahdi a matsayin mataimakin gwamnan Zamfara

Date:

Daga Maryam Ibrahim Muhammad

 

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, a yau Laraba, ta ba da umarnin mayar da Mahdi Ali Gusau a matsayin mataimakin gwamnan jihar Zamfara, biyo bayan tsige shi da majalisar dokokin jihar ta yi a ranar 23 ga watan Fabrairun 2022, duk kuwa da umarnin kotu na hani da cire shin.

 

Sai dai kuma Mai shari’a Inyang Ekwo, a hukuncin da ya yanke, ya kuma rushe duk wani mataki da majalisar ta dauka, da tsohon Gwamna Bello Matawalle da alkalin alkalan jihar na tsige Gusau a lokacin da ake shigar da kara a gaban kotu.

Za’a karawa Tinubu da sauran shugabanni a Nigeria Albashi

Mai shari’a Ekwo, wanda ya ce abin da kakakin majalisar na wancan lokacin, tsohon gwamna, babban alkalin alkalai da sauran su suka yi, ya zama maras amfani yanzu, ya bayyana shi a matsayin “ rusashshe kuma ba shi da wani tasiri.”

Tallah

Ekwo ya ce shi bai ga dalilî da hujjoji na shari’a da za su sanya a tsige mataimakin gwamnan ba.

Sai dai kuma Daily Nigerian Hausa ta fahimci cewa duk da kotu ta mayar da shi, Mahdi ba shi da ikon zama Mataimakin Gwamna a halin yanzu tun da ba da shi a ka yi zaɓen 2023 ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...