Kungiyar tsofaffin Daliban MAAUN ta wayar da kan dalibai mata hanyoyin da zasu kare kansu daga cututtuka

Date:

Daga Abdulmajid Habib Isa Tukuntawa

 

Kungiyar tsofaffin dalibai jami’an Maryam Abacha da suka yi karatun aikin jinya wato Nursing Association of MAAUN ta kai wata ziyara ta wayar da kan daliban makarantar mata ta Kano Capital Girls Secondary School .

 

Da yake yiwa wakilin Kadaura24 karin bayani kakakin kungiyar Sadiq Abubakar Ado yace sun shirya taron wayar da kan matan ne domin sanar da su hanyoyin da zasu kare kansu daga cututtuka musamman masu yaduwa.

 

” Da yake mata suna jinin al’ada to akwai bukatar matan su San yadda zasu kula da kansu saboda lokaci ne da zasu iya daukar cututtuka saboda yanayin halittarsu”. Inji Sadiq Ado

Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya bayyana ranar da zai mikawa majalisa sunayen kwamishinonini

Yace mata da yawa su kan dauki cututtuka a bandaki wato UTI Impection wanda hakan yakan haifar musu da matsalolin, hakan ce tasa suka je makarantar domin wayar da kan su don su gojewa duk abubuwan da ka iya haifar musu da matsala.

 

” Wannan aiki da mukai na tallafawa al’umma Mai makarantar mu ta MAAUN Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo saboda mutum ne Mai tallafawa al’umma shi yasa muka ga dacewar mu yi koyi da shi daidai karfinmu tunda ba za mu iya yin yadda yake yi ba”. A cewar kakakin kungiyar

Gwamnatin Kano za ta rushe Masarautun Gaya, Rano, Bichi da Karaye da Kuma dawo da Sarki Sunusi

Sadiq Abubakar Ado ya kara da cewa a lokacin watan Ramadana sun kai tallafi gidan marayu, shi yasa a wannan karon suka kai wancan tallafi makarantar Kano Capital, Inda suka raba audugar mata ga mata 50 .

Wakiliyar shugabar makarantar ta kano Capital Hajiya Maimuna Nuhu tace sunyi farin ciki da zuwan wannan kungiya makarantar da suka yadda suka wayar da kan daliban da Kuma kayan da suka raba musu

Wasu daga cikin daliban da suka amfana

“Ya kamata sauran kungiyoyin tsofaffin dalibai su yi koyi da kungiyar tsofaffin daliban jami’ar MAAUN don tallafawa al’umma da ilimin da suka samu da Kuma dan abun da suke da shi”. A cewar Maimuna Nuhu

Hajiya Maimuna Nuhu ta yi fatan kungiyar baza ta gajiya ba wajen yin irin wannan aikin alkhairi, sannan ta hori daliban da su yi amfani da ilimin da suka samu don kare kawunansu daga kamuwa da cututtuka.

Suma wasu daga cikin daliban da suka samin tallafin sun nuna farin cikin tare da godewa wannan kungiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...