Majalisa ta 10: Jam’iyyar PDP ta yi zargin ana shirin kama ‘Yan Majalisarta

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Aliyu

 

Jam’iyyar PDP ta koka kan wani shiri na kama wasu zababbun ‘yan majalisarta da ke neman ‘yancin cin gashin kansu akan rikicin zabar shugabancin majalisar kasa ta 10.

 

Da yake jawabi ga manema labarai a hedikwatar jam’iyyar a jiya, sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba, ya ce tanade-tanaden majalisun biyu ya jaddada bukatar barin ‘yan majalisar su zabi shugabanninsu da kansu ba tare da tsuma bakin wasu daga wajen majalisar ba.

Da dumi-dumi: Kwankwaso ya bayyana abubuwan da suka tattauna da Shugaba Tinubu

Ya kuma bayyana cewa ‘yancin ‘yan majalisa wani abu ne mai matukar muhimmanci a tsarin dimokuradiyya da kundin tsarin mulki, inda ya kara da cewa ‘yancin majalisa na zabar Shugabannin su tsari ne mai zaman kansa a tsarin dimokuradiyya.

Ya ce tun lokacin da jam’iyyar PDP ta bayyana matsayinta na cewa tana da sha’awar shugabancin majalisar ta 10, ake ta yunkurin tursasawa, muzgunawa da kuma yi wa zababbun ‘yan majalisar barazana da nufin yiwa yunkurin nasu kafar angulu don kar su sami shugabancin majalisar.

Jam’iyyar PDP ta kara da cewa ‘yancin ‘yan majalisa wani sharadi ne a dimokuradiyya wanda indai dimokuradiyya ake so dole baiwa duk dan majalisar damar shiga ya zaba ko a zabe shi a cikin shugabancin majalisar . inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...