Sarkin Kano ya taya Abba Gida-gida Murnar lashe zaben gwamnan jihar

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero CFR, JP ya taya Zabbben Gwamnan Jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf Murna bisa nasarar da ya samu ta lashe zaben Gwamnan Kano a zaben da aka gudanar ranar Asabar din data gabata 18th ga wannan wata na Maris.

 

Cikin wata sanarwa daga Sakataren Yada Labarai na Masarautar Kano Abubakar Balarabe Kofar Naisa ta bayyana cewa al’ummar kasar nan sun karbi tsarin mulkin damokaradiyya da matuqar muhimmacin idan akayi la’akari da yadda suka futo domin jefa kuri’unsu kamar yadda tsarin mulki ya bada dama.

 

Ku dakatar da tattakin da ku ke yi don nasarar da mu ka samu, maimakon haka ku yi mana addu’a-Abba Gida-gida

Sanawar ta kuma godewa malamai da Limamai da sauran Al’umma bisa addu’ar zaman lafiya da suka dunga yi kafin da kuma bayan gudanar da zaben.

 

Daga nan fadar Masarautar ta Kano tayi nasiha tare da kira ga sabon gwamnan daya hada kai da dukkanin rukunin al’umma wajen tafiyar da gwamnati, domin yin hakan zai taimaka wajen kyautata rayuwar al’umma da kuma kawo cigaban da ake bukata domin bunkasar tattalin arziki ga jihar Kano da kasa baki daya.

Gawuna ya taya al’ummar musulmi shigowa watan Ramadan

 

Alhaji Aminu Ado Bayero yayi fatan dorewar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Kano har ma da sauran sassan kasar nan.

 

yayi addu’ar fatan kammala tenure mulkinsa lafiya tareda samun cigaban gwamnatinsa da habaka tattalin arzikin jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...