Sifeto-Janar ya kawo sabon Kwamishinan Ƴansanda Kano

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

 

Sufeto-Janar na ƴansanda, IGP Usman Alkali ya fasa kawo Balarabe Sule, tsohon babban jami’in tsaro na gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje, zuwa jihar domin gudanar da zabe.

 

Yanzu haka dai IGP din ya mayar da CP Faleye Olaleye daga jihar Ebonyi zuwa Kano domin ya jagoranci rundunar a lokacin zabe.

 

IGP din ya kuma sake tura karin wasu manyan jami’ai zuwa jihar domin karfafa tsaro a lokacin zabe.

 

Kamar yadda jaridar DAILY NIGERIAN ta gani na baya-bayan nan, IGP din ya tura AIG Sani Dalijan domin ya jagoranci shiyya ta daya a Kano.

 

Haka kuma takardar ta nuna cewa Ita Lazarus Uko-Udom ne zai jagoranci Kano ta tsakiya, inda DCP Umar Iya zai kasance na biyu a matsayin shugaba.

 

Alkali ya kuma aike da DCP Abdulkadir El-Jamel domin kula da kananan hukumomin Albasu, Gaya, Rogo, Takai, Ajingi, Garko, Wudil da Sumaila.

 

A kananan hukumomin Rano, Bebeji, Bunkure, Doguwa, Kiru, Kibiya Tudunwada dake jihar Kano ta kudu kuwa, IGP ya tura DCP Adamu Ngojin domin ya kula da tsaron a can haka.

 

IGP din ya kuma tura DCP Abaniwonda Olufemi zuwa Kano ta Arewa, tare da ACP Adamu Sambo a matsayin babban kwamandan sa na biyu.

 

Kamar yadda sabuwar takardar ta nuna, DCP Auwal Musa ne zai jagoranci CID, yayin da DCP Aminu Maiwada zai dauki nauyin gudanar da ayyuka a hukumar ta Kano a lokacin zabe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...