Mun haɗa tawagar lauyoyi 19 domin ƙalubalantar Nasarar Tinubu a Kotu – Atiku

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Ɗan takarar shugaban Najeriya na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya haɗa tawagar manyan lauyoyi 19 domin ƙalubalantar sakamakon zaɓen da aka yi na ranar 25 ga watan Fabarairu.

 

Atiku ya yi wa lauyoyin bayani a yau Laraba a hedikwatar yaƙin neman zaɓensa a Abuja, inadl ya buƙace su da su tabbatar wa da kotu dokokin da aka keta a zaɓen tare da sake ƙwato abin da ya kira ikon ‘yan Najeriya.

 

Tawagar na ƙarƙashin jagorancin ƙwararren lauya mai zaman kansa JK Gadzama.

 

Ɗantakarar ya sheda musu cewa abu ne mai muhimmancin gaske su tabbatar sun tsaya tsayin daka domin tabbatar da nasara a shari’ar ba saboda shi ba kawai da PDP, domin ma sake tabbatar da dumukuraɗiyya domin ƴan gaba.

 

Tarin manyan lauyoyin sun haɗa da Chief Chris Uche da Paul Usoro da Tayo Jegede da Ken Mozia da Chief Mike Ozekhome da Mahmood Magaji da Joe Abraham da Chukwuma Umeh da Garba Tetengi da kuma Chief Emeka Etiaba.

 

Akwai kuma Chief Goddy Uche da Farfesa Maxwell Gidado da mai bayar da shawara kan shari’a na na ƙasa na PDP A.K. Ajibade da O.M. Atoyebi da Nella Rabana da Paul Ogbole da Nuremi Jimoh da kuma Abdul Ibrahim.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...