INEC ta Sanya ranar da zata baiwa Sanatoci da ‘Yan Majalisu Takardun Shaidar lashe zabe

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta ce ‘yan takarar da aka zaba a majalisar dattawa da ta wakilai a zaben na ranar Asabar da ta gabata za su karbi takardar shaidar cin zabe a mako mai zuwa.
 Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya sanar da hakan a ranar Asabar a wani taro da suka yi da kwamishinonin zabe, a Abuja.
 A cewar Yakubu, za a baiwa zababbun Sanatoci satifiket din su ne a ranar 7 ga Maris, yayin da takwarorinsu na Majalisar Wakilai za su karbi nasu a ranar 8 ga Maris.
 Shugaban na INEC ya kuma bayyana cewa an bayyana sunayen wadanda suka yi nasara a kan kujeru 423 na ‘yan majalisa, inda ya kara da cewa an bayyana karin zaben a mazabu 46.
 An bayyana cewa, kujeru 98 daga cikin kujeru 109 na majalisar dattawa da kuma kujeru 325 daga cikin kujeru 360 na majalisar wakilai an bayyana wadanda suka lashe zabukan su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...