Ƴan sanda sun kama waɗanda ake zargi da yunkurin ƙona ofishin INEC a Kano

Date:

Rundunar ƴan sanda a Kano ta ce ta kama mutum huɗu da ake zargi da yunkurin ƙona ofishin hukumar zaɓe a karamar hukumar Takai na jihar.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun ƴan sandan jihar SP Abdullahi Kiyawa ya fitar, ta ce ana zargin mutanen huɗu da yunkurin ƙona ofishin na INEC a daidai lokacin da ake sanar da sakamakon zaɓe.

BBC Hausa ta rawaito Sanarwar ta ce ƴan sandan sun samu nasarar kama mutanen ne bayan kai samamen gaggawa tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro.

Haka ma, ƴan sanda sun ce wasu ƴan bangar siyasa sun kai hari kan ofishin yakin neman zaɓe na jam’iyyar NNPP a karamar hukumar Tudun Wada, inda aka kashe mutum biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwankwaso ya yi tsokaci game da zaben cike gurbi da akai a Kano

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana...

A Hukuma ce INEC ta bayyana sakamakon zabukan cike gurbi da aka yi a kano

Hukumar zabe mai zamanta ta Kasa ta bayyana Dan...

PDP ta yi watsi da zaben cike gurbi na Bagwai da Shanono dake Kano

Jam’iyyar PDP reshen jihar Kano Arewa maso Yammacin Najeriya...

Jam’iyyar APC ta bayyana matsayarta kan zaben cike gurbi a Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...