Bai kamata CBN ya sauya fasalin kuɗi a wannan gabar ba – Tinubu

Date:

Daga Auwalu Alhassan Kademi

 

Kwamitin Yaƙin neman Zaben dan takarar shugaban ƙasa na APC, PCC, ya ce bai kamata Babban Bankin Najeriya (CBN) ya sake tsara fasalin Naira a wannan lokacin ba.

 

Bayo Onanuga, Daraktan watsa labarai da wayar da kan jama’a na kwamitin ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a jiya Juma’a a Abuja.

 

“Manufar sake fasalin naira ta zama wani nauyi da ‘yan Najeriya ba za su iya dauka ba,” in ji Onanuga, inda ya kara da cewa ‘yan Najeriya da dama na shan wahala wajen karbar kudadensu daga asusun su saboda manufar.

Talla

Ya caccaki tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar kan adawa da kiran da CBN ya yi na kara wa’adin musanyar kudin naira a ranar 10 ga watan Fabrairu.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

“Yin zagon kasa da canjin kudi na Naira da karancin man fetur a sassan kasar nan ya janyo wa miliyoyin ‘yan Najeriya wahala.

 

“Ci gaban ya bayyana hakikanin halin PDP da Atiku a matsayin makiyin jama’a lamba daya.

 

“Tun da CBN ya gabatar da manufofin musanya kudi da kuma sabbin tsare-tsare na Naira, Atiku Abubakar da PDP sun yi shiru na mugunta.

 

Onanuga ya ce, “hakan ya nuna cewa su na amfana da rashin jin dadin manufofin da za su haifar wa ‘yan Najeriya da kuma bacin ran da zai haifar wa APC,” in ji Onanuga.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...