Yanzu-yanzu: Bankuna za su ci gaba da karɓar tsoffin kuɗaɗe har bayan ƙarewar wa’adi – CBN

Date:

Daga Kamal Umar Kurna

 

Gwamnan Babban Bankin Ƙasa, CBN, Godwin Emefiele, ya ce bankuna za su ci gaba da karbar tsoffin takardun kudi na Naira har bayan wa’adin musanya wa da sabbin kudi ranar 10 ga Febrairu.

 

A ranar Lahadi ne babban bankin ya kara wa’adin rufe karɓar tsoffin takardun Naira na 1,000 da 500 da kuma N200, biyo bayan korafin ‘yan Najeriya.

Talla

Sai dai a yayin da Emefiele ya bayyana a gaban kwamitin majalisar wakilai kan sabon tsarin sauya fasalin Naira ,da kuma canjin naira a yau Talata, shugaban na CBN ya ce har yanzu bankuna za su karbi tsoffin takardun har bayan wa’adin.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Emefiele ya ce idan aka yi la’akari da sashe na 20, karamin sashe na 3 na dokar CBN ta 2007, ko da wa’adin amfanin tsoffin kuɗaɗe ya cika, CBN za ta ci gaba da karbar su.

 

Emefiele ya ce dole ne bankunan kasuwanci su karbi kudin ko da bayan wa’adin 10 ga watan Fabrairu ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...