Daga Kamal Umar Kurna
Gwamnan Babban Bankin Ƙasa, CBN, Godwin Emefiele, ya ce bankuna za su ci gaba da karbar tsoffin takardun kudi na Naira har bayan wa’adin musanya wa da sabbin kudi ranar 10 ga Febrairu.
A ranar Lahadi ne babban bankin ya kara wa’adin rufe karɓar tsoffin takardun Naira na 1,000 da 500 da kuma N200, biyo bayan korafin ‘yan Najeriya.

Sai dai a yayin da Emefiele ya bayyana a gaban kwamitin majalisar wakilai kan sabon tsarin sauya fasalin Naira ,da kuma canjin naira a yau Talata, shugaban na CBN ya ce har yanzu bankuna za su karbi tsoffin takardun har bayan wa’adin.

Emefiele ya ce idan aka yi la’akari da sashe na 20, karamin sashe na 3 na dokar CBN ta 2007, ko da wa’adin amfanin tsoffin kuɗaɗe ya cika, CBN za ta ci gaba da karbar su.
Emefiele ya ce dole ne bankunan kasuwanci su karbi kudin ko da bayan wa’adin 10 ga watan Fabrairu ne.