Tallafawa Marayu a sha’anin karatu ginshiki ne na samar da al’umma ta gari -Shugaban K/H Fagge

Date:

Daga Kamal Umar Kurna

 

Shugaban karamar hukumar fagge Honourable Ibrahim Abdullahi Muhd Shehi ya bayyana taimakawa marayu da tallafar yaran da iyayensu keda karamin karfi da kayan koyon karatu da koyarwa a matsayin wani ginshiki wanda zai haifar da al’amma ta gari.

 

Shugaban wanda ya samu wakilcin Alhaji Murtala Tijjani, ya bayyana hakan ne wajen rabawa daliban makaratun firamare 300 wadanda suka fito daga karamar hukumar fagge kayan sawa na makaranta wato Uniform da litattafai da kuma rabawa marayu 70 tallafin kudi naira dubu biyar biyar ga kowannensu wanda gidauniyar daya daga cikin ‘yan kishin karamar hukumar ta fagge Abdulaziz Mohd Abdullahi wanda aka fi sani da Malam wato Me Lamma foundation ta shirya a hedkwatar hisbar karamar hukumar.

 

Talla

Da yake jawabi tunda farko Hakimin Fagge Tafidan Kano Alhaji Mahmud Dr Ado Bayero wanda ya samu wakilcin dagacin rijiyar lemo Alhaji Nazifi Hamidan Abdulkarim ya bayyana cewa matashi dama shi ne kan gaba a kowace nahiya musamman karatun firamare daga tushe, wanda hakan ya zama wajibi a yabawa gidauniyar ta Me lamma.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Da yake ta’aliki akan makasudin daya sanya shi assasa bada tallafin, shugaban gidauniyar ta Me Lamma Abdulaziz Mohd Abdullahi wato Malam yace taimakawa masu karamin a kowace fuska musamman ilimi da marayu zai samar da ingantacciyar al’umma.

 

Daga cikin makaratun da suka rabauta da tallafin akwai makarantar firamare ta Gobirawa project , da kwachirin jobe firamare, da Na tsugunne firamare da Yusif Ata firamare sai kuma kurna firamare dukkaninsu a karamar hukumar ta fagge.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...