Za mu ɗauki ma’aikata miliyan 1.4 don gudanar da aikin zaɓe – INEC

Date:

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya ta bayyana cewa za ta ɗauki ma’aikatan wucin-gadi kimanin miliyan 1.4.

 

Waɗanda suka haɗar da masu yi wa ƙasa hidima da ɗaliban manyan makarantun ƙasar da ke shekarar ƙarshe domin taimaka mata gudanar da aikin babban zaɓen ƙasar da ke tafe.

 

Babban kwamishina a hukumar zaɓen kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da ilimantar da masu kaɗa kuri’a na hukumar Festu Okoye ne ya bayyana haka ta cikin shirin gidan Talbijin ɗin Arise TV mai suna Morning Show.

Talla

Haka kuma hukumar ta gargaɗin masu sayen ƙuri’un mutane da masu ƙirƙirar lambobin katin zaɓen da su daina aikata hakan.

 

Domin kuwa a cewarsa akwai bayanan kowanne kati a kan na’urarsu ta tantance masu kaɗa lkuri’a, dan haka sayen kuri’ar ba zai amfanar da su da komai ba.

 

Sai ma cutar da ainihin masu katunan na hana su yancinsu da kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba su na jefa kuri’a a ranar zaɓen.

 

Mista Okoye ya ƙara da cewa ”mun bayyana ƙarara cewa hukumarmu za ta kai na’aurar tantance masu kaɗa kuri’a a rumfunan zaɓe, domin tantance masu zaɓe, kuma bayanan kowa na ƙunshe cikin na’urar, a maimakon jikin katin zaɓen”.

Tallan Garin dan wake mai inganci

”Dan haka abin da kawai jami’in zaɓe zai yi ranar zaɓe shi ne duba lambobi shidan ƙarshe da ke jikin katin zaɓenka, domin fito da bayananka daga cikin na’urar tantace masu kaɗa kuri’ar”.

 

”Dan haka masu sayen kuri’ar da masu kirkirar lambobin kati za su cutar da masu katunan ne kawai. Ta hanyar hana su yin zaɓe, amma dan ɗaukar katin wani domin bai wa wani ya yi amfani da shi a ranar zaɓe wannan sam ba abu ne mai yiyuwa ba”

 

A ranar 25 ga watan Fabairun wannan shekarar ne dai za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...