Abdulmumini Kofa ya raba Jarin Naira Miliyan 50 ga Mutanen Kiru da Bebeji

Date:

Daga Zakaria Adam Jigirya
Dan takarar majalissar tarayya na kananan hukumomin Kiru/Bebeji a jam’iyyar NNPP Hon Abdulmumin Jibrin Kofa PhD,(Jarman Bebeji) ya gwanjage wasu daga cikin mutanen yankinsa da tallafin jari na kudade.
An dai gudanar da bikin bada tallafin ne a gidansa dake garin kofa a Karamar hukumar Bebeji.
Yayin da yake jawabi a wajen taron Abdulmumini Kofa ya ce ya basu jarin ne a wani bangare na yakin da yake yi da zaman kashe wanda da kuma inganta masu Kananan sana’o’i.
Talla
” Mun jima Muna bayar da  irin wannan tallafin da zaku iya tunawa ma a ranar 1 ga watan 1 na shekarar 2022 sai na muka hadu anan mukai addu’o’i sannan na baiwa wasunku jari, Kuma babu shakka haka zamu cigaba da yi har sai mun fatattaki talauci a kananan hukumomin Kiru da Bebeji.” Inji kofa
Abdulmumini Jibril kofa ya kuma bada tabbacin zai cigaba da tallafawa al’ummar yankin, musamman idan ya samu nasarar lashe zaben wannan shekara ta 2023.
 wasu sun rabauta da Dubu dari biyu(#200,000), Dubu dari daya(#100,000), Dubu Hamsin(#50,000), Dubu Ashirin(#20,000), Dubu Goma(#10,000) da kuma Dubu Biyar(#5,000).
Tallan Garin dan wake mai inganci
Mutanen da suka amfana da wannan jari/tallafi sun hada da wakilan akwatuna, Exco na karamar hukuma da mazabu na Jam’iyyar NNPP da PDP na Kiru/Bebeji, KOKAS na Kiru/Bebeji, Wasu kungiyoyi masu karfi na mata da matasa a Kiru/Bebeji, Dagatan Kiru/Bebeji, Limaman Juma’a Kiru/Bebeji, Malaman Kwankwasiyya Kiru/Bebeji, Dalibai, Yan Social Media, Mafarauta, Yan Achaba, Mahauta da kuma mutane masu bukata ta musamman.
Wannan taro ya sami halartar yan takarkaru na Kiru/Bebeji, manyan jagorori tare da shuwagabannin jam’iyyar NNPP/PDP na Kiru/Bebeji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...