Gine-gine kimanin 5,000 aka rushe wadanda aka yi a ƙarƙashin manyan layukan lantarki a Najeriya

Date:

 

Shugaban hukumar kula da harkokin wutar lantarki a Najeriya ta Nigerian Electricity Management Service Agency (NEMSA) ya ce sun rusa gine-gine kusan 5,000 da ke ƙarƙashin manyan wayoyin lantarki a faɗin ƙasar.

 

Aliyu Tahir wanda shi ne kuma babban jami’in lantarki na ƙasa, ya faɗa a yau Juma’a cewa tun 2017 aka ɗauki mataki tare da ba da umarnin rushe gine-ginen da ke ƙarƙashin wayoyin, kamar yadda kamfanin labarai na NAN ya ruwaito.

 

NEMSA ta ce akwai buƙatar gaggauta katse yankunan daga layin lantarki da kuma rushe su daga baya.

Talla

 

“A ɓangarenmu, mun bai wa kamfanonin rarraba lantarki umarnin sauke duk wani gini da aka yi a ƙarƙashin babban layin lantarki daga kan layin wutar, har ma da waɗanda suka tare hanya,” a cewarsa.

 

Tahir ya ƙara da cewa rushe gine-ginen na buƙatar himma daga waɗanda abin ya shafa, “kamar gwamnatin tarayya da ta jihohi”.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...