Daga Aisha Aliyu Umar
Mataimakin gwamnan jihar kano Dr Nasiru Yusuf Gawuna yace nan da jimawa kadan zata zauna domin sake yin duba kan sabuwar dokar hana yan adaidaita sahu bin wasu manyan tituna a Kano .

” Mun sami labarin halin da al’umma suka shiga sakamakon Wannan doka, yanzu haka gwamnati ta bada dama a sake duba dokar don samar da abun da bazai musgunawa al’umma ba”.
Mataimakin gwaman ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin ranar larabar nan.
Yace gwamnati ta tura jami’ai domin duba halin da al’umma suka shiga, Kuma ta ji koke -koken al’umma, zata ɗauki matakan saukakawa al’umma tunda dama gwamnatin ta al’umma ce .
” Duk abun da ya kamata a yi in Allah ya so nan da zuwa an jima kadan gwamnati ta sahale mu zauna mu duba mu gani, domin a kawo masalahar Wannan al’amarin, Kuma Ina tabbatarwa al’umma cewa bi’izinin lahi za’a yi abun da al’umma zasu ji dadin sa”. Inji Gawuna