Ƴan Sanda sun kama wani jigon jam’iyyar NNPP a Kano

Date:

Daga Maryam Adamu Mustapha

 

Rahotanni sun bayyana cewa ƴan sanda sun kama Ambasada Yusuf Imam, wanda a ka fi sani da Ogan Boye, ƙusa a jam’iyyar adawa ta NNPP a jihar Kano.

 

Wani makusancin Ogan boyen wanda ya nemi a sakeye sunansa shi ne ya bayyana mana cewa an kama Ogan Boye ne tun a daren jiya Lahadi a gidansa da ke Ƙaramar Nassarawa, inda su ka kai shi shelkwatar rundunar.

Talla

Har yanzu dai ba a san dalilin da ya sa a ka kama Ogan Boye ba, sai dai Wani makusancin Ogan boyen ya shaida mana cewa hakan ba ya rasa nasaba da rigingimn siyasa da su ka fara kunno kai tsakanin APC da NNPP a jihar.

 

Sai dai kuma da wakilin Kadaura24, ya kira mai magana da yawun rundunar ƴan sandan, bai samu daga wayar ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...