Nigeria@62: Ganduje ya jinjinawa wadanda suka taba yin gwamna a kano

Date:

Gwamnan jihar kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya kalubalanci al’ummar Nigeria da su zauna lafiya da juna domin cigaban kasar baki daya.
 Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga al’ummar jihar nan a yayin bikin cikar Nijeriya shekaru 62 da samun ‘yancin kai wanda ya gudana a filin wasa na Sani Abacha Kano.
 Yace akwai bukatar ‘yan Nigeriya su zauna da juna lafiya a matsayin ‘yan’uwa ba tare da la’akari da addini ko bambancin kabila ba.
Talla
Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa gwamnatinsa ta samu nasarori da dama ta fuskar samar da ababen more rayuwa da samarwa matasa aiyukan yi da inganta fannin kiwon lafiya, ilimi da noma.
 Ya kara da cewa nan ba da jimawa ba za a kammala ginin cibiyar cutar masu ciwon daji ta zamani yana mai ba da tabbacin cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kaddamar da sabon Asibitin .
 Gwamnan ya shawarci al’ummar jihar da su guji siyasar ‘yan daba da tashe-tashen hankula, Ya roke su da su rungumi tsarin dimokuradiyya na juriya da zaman lafiya don cigaban kasar nan.
Talla
” Da yake wannan shi ne jawabina na karshe gareku a matsayi na na Gwamnan kano, ina kira ga al’ummar jihar kano da su zabi shugabannin na gari irinsu Dr. Nasiru Yusuf Gawuna Wanda nayi imani idan kuka zabe shi zai kara ciyar da Kano gaba tunda duk abun da makai da shi muka yi”.
Ganduje ya kuma yabawa dukkanin wadand sukai yi gwamna a Kano saboda irin gudunmawar da dukkaninsu suka bayar wajen cigaban jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani...

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Daga Nazifi Dukawa   Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar...