Bama fatan gwamnati mai zuwa ta zama irin ta Buhari – Umma Getso

Date:

Daga Kabiru Muhammad Get so

 

Tsohuwar ‘yar takarar mataimakiyar Shugaban kasa a jam’iyyar YPP Hajiya Umma Getso ta bayyana cewar yanzu haka al’ummar kasar nan na cikin wani irin hali tare da fatan samun sabuwar Gwamnati Da zata fi wannan Gwamnati da muke cikin ta Buhari.

 

Umma Getso ta bayyana haka ne lokacin da take ganawa da manema labarai a dai dai lokacin da ake murnar tunawa da ranar samun ‘yancin kai.

 

Tace babu wata riba da aka samu a wannan Gwamnati musamman idan akayi la’akari da matsalar tsaro,fatara da karuwar rashin aikin yi ga matasa.

Talla

Umma Getso wacce take daya daga cikin mata ‘yan Gwagwarmaya masu fafutukar kawo sauyi a kasarnan, tace duk da yanzu ta fita daga ‘yamiyyar da tayi takara a baya babu shakka zata yi duk Mai yiwuwa wajen wayar da kan Al’umma musamman mata domin zaban Jam’iyyar da ta dace da kawo sauyi a kasarnan.

 

KaZalika tayi kira ga mata da matasa da kada su bari ayi amfani dasu wajen tada zaune tsaye a wajen yakin neman zabe.

Talla

Maimakon hakan kamata yayi subi matakai daban daban wajen zabar wadanda zasu taimakesu da kuma dawo da kasar bisa kyakkyawan tsarin da zai canda yanayin kasarmu Nigeria.

Ta kara ta cewar abun takaicine ace Nigeria tana da shekaru 62 amma har yanzu Ana kallon kamar har gara ma lokacin kasar tana hannun turawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...