Za a rage sadaki da kudin biki a China

Date:

Daga Khadija Abdullahi

 

Gwamnatin China ta kaddamar da wani gangami na rage yawan kudin da ake kashewa a yayin biki da kuma rage sadaki.

Gwamnatin ta yi hakan ne a wani bangare na yunkurin dakatar da raguwar da ake samu a yawan masu aure abin da kuma ya janyo raguwar haihuwa.

Talla

Kungiyoyi da dama ne suka shiga gangamin, da nufin janyo hankalin mutane a kan rage almubazzaranci yayin biki.

 

Gwamnatin ta ce idan an rage yawan kudin da ake kashewa a lokacin biki za a samu karuwar masu yin aure a kasar.

Talla

 

To sai dai kuma masu sharhi sun ce da wuya wannan yunkuri ya yi tasiri, saboda raguwar da al’ummar kasar ke yi ya sa mutane kalilan ne zasu kai shekarun aure.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano ya Naɗa Ahmed Musa a Matsayin Janar Manaja na Kano Pillars

Daga Zakaria Adam Jigirya   Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Yanzu:yanzu: Gwamnan kano ya yi sabbin nade-naden mukamai

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Gwamann jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...