Kano ta tsakiya: Shekarau da Kwankwaso har yanzu bakin su daya – Musa Iliyasu Kwankwaso

Date:

Daga Abubakar Sadeeq

 

Ɗan takarar majalisar tarayya a ƙananan hukumomin Kura, Madobi da Garun Malam a jam’iyyar APC, Hon Musa Iliyasu Kwankwaso ya ce tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau da takwaransa Engr. Rabiu Musa Kwankwaso sun haɗa kai ne domin ruguza jam’iyyar NNPP domin su marawa Atiku Abubakar da Bola Tinubu baya a kakar zaben 2023.

 

Musa Iliyasu Kwankwaso ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da yayi da wakilin jaridar Kadaura24 a ranar Larabar nan.

 

Talla

Yace bayyana sunayen yan takarar sanatoci da majalisar tarayya, da hukumar zaɓe ta yi a jiya talata, ya tabbatar da cewa kwankwaso da malam shekarua na shirin yin Abu daya a zaben shekara ta 2023.

 

“ jam’iyyar NNPP mai Mayan gwari bata da ɗan takara a sanatan Kano ta tsakiya, domin sunan Shekarau aka bayyana”. Inji kwankwaso

 

 

Talla

 

Ya kara da cewar “akwai tabbacin Kwankwaso Bola Ahmad Tinubu zai marawa baya, kuma duk abin nan da ya faru haɗin bakin kwankwaso da Shekarau don jam’iyyar ta ruguje, sai da suka yi shawara da Kwankwaso don jam’iyyar ta yi biyu babu”.

 

Musa lliyasu kwankwaso yace shekarau da kwankwaso suna sane da cewa INEC zata fitar da takarar sunan shekarau a matsayin Dan takarar sanatan kano ta tsakiya bayan ya fice daga NNPP zuwa PDP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani...

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Daga Nazifi Dukawa   Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar...

Da dumi-dumi: Bayan dakatar da Sojaboy daga Kannywood, wata masarautar a sokoto ta tube rawaninsa

Masarautar Gidan Igwai ta dakatar da Usman Umar wanda...

Masu yada hotunan Akpabio a ofishin SDP suna yi ne don bata sunan Jam’iyyar – Hon. Ali Shattima

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban Jam'iyyar SDP na jihar Kano...