Yan China Mazauna Jihar Kano Sun yi Allah Wadai da Kisan Ummita

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Yan china mazauna jihar kano karkashin jagorancin Shugaban su Mr. Mike Zhang sun yi Allah Wadai da kisan da wani Dan China yayi wa Ummulkhairi Buhari dake unguwar jan bulo a birnin kano.

Talla

Kadaura24 ta rawaito Cikin wata Sanarwar da hadinmin wakilin yan China a jihar Kano Mr. Guang Lei Zhang ya fitar a madadin dukkanin yan china mazauna jihar kano sun ce basa goyon bayan ta’addancin da guda daga cikin su yayi na kisan Ummita har gida.

Abin da Ummita ta gaya min a kan saurayinta ɗan China da ya kashe ta — Sheikh Daurawa

 

Sun Kuma ce kisan ta’addancin ne wanda bai kamata a bar wanda yayi shi hakan nan ba, Inda suka yi kira ga Hukumomin tsaro da su tabbatar an hukunta wanda yayi laifin dai-dai da dokar Kasar nan.

Ganduje yace dole doka ta yi aiki akan dan Chinan da ya kashe Ummita

Sanarwa tace dukkanin yan china mazauna jihar kano sun goyon bayan a hukunta wanda yayi kisa domin ya zama izina ga duk masu hali ko tunani irin nashi, sannan suka yabawa al’ummar jihar nan bisa karrama da karbar baki da suke yi a koda yaushe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano ya Naɗa Ahmed Musa a Matsayin Darakta Janar na Kano Pillars

Daga Zakaria Adam Jigirya   Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Yanzu:yanzu: Gwamnan kano ya yi sabbin nade-naden mukamai

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Gwamann jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...