NDLEA ta kama kwalaben Akurkura 26,600 a Kano

Date:

Daga Aliyu Abdullahi Danbala Gwarzo
Jami’an hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi, NDLEA, sun kama wani fitaccen mai haɗa wani abin sha da ke taɓa ƙwaƙwalwa, wanda aka fi sani da Akurkura a Kano.
Jami’an NDLEA ɗin sun cafke Qasim Ademola, inda su ka damƙe kwalabe 26, 600 na kayan mayen da aka tanada domin rabawa a fadin jihohin Arewa.
An kama kayan ne a ranar Alhamis, 15 ga watan Satumba a kan hanyar Zaria zuwa Kano, Gadar Tamburawa.
Talla
A nan ne kuma a ka cafke mai haɗa sinadarin, mai shekaru 39 ɗan karamar hukumar Akinyele, jihar Oyo da uku daga cikin masu rarraba shi a wani samame da aka yi.
Shugaban Hukumar NDLEA, Buba Marwa, ya yabawa hafsoshi da jami’an rundunar a Kano bisa yadda suke ƙwazo da jajircewa wajen gudanar da ayyukan su.
Talla
Ya kuma umarce su da sauran su a fadin kasar da su ci gaba da mai da hankali yayin da suke sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano ya Naɗa Ahmed Musa a Matsayin Janar Manaja na Kano Pillars

Daga Zakaria Adam Jigirya   Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Yanzu:yanzu: Gwamnan kano ya yi sabbin nade-naden mukamai

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Gwamann jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Yara ɗalibai na fuskatar barazanar daina zuwa Makaranta a Hotoro saboda lalacewar hanya

Daga Isa Ahmad Getso   Al'umma da Malaman makaranta a unguwar...

Kotu ba da umarnin mayar da Natasha bakin aikinta

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Majalisar...