NDLEA ta kama kwalaben Akurkura 26,600 a Kano

Date:

Daga Aliyu Abdullahi Danbala Gwarzo
Jami’an hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi, NDLEA, sun kama wani fitaccen mai haɗa wani abin sha da ke taɓa ƙwaƙwalwa, wanda aka fi sani da Akurkura a Kano.
Jami’an NDLEA ɗin sun cafke Qasim Ademola, inda su ka damƙe kwalabe 26, 600 na kayan mayen da aka tanada domin rabawa a fadin jihohin Arewa.
An kama kayan ne a ranar Alhamis, 15 ga watan Satumba a kan hanyar Zaria zuwa Kano, Gadar Tamburawa.
Talla
A nan ne kuma a ka cafke mai haɗa sinadarin, mai shekaru 39 ɗan karamar hukumar Akinyele, jihar Oyo da uku daga cikin masu rarraba shi a wani samame da aka yi.
Shugaban Hukumar NDLEA, Buba Marwa, ya yabawa hafsoshi da jami’an rundunar a Kano bisa yadda suke ƙwazo da jajircewa wajen gudanar da ayyukan su.
Talla
Ya kuma umarce su da sauran su a fadin kasar da su ci gaba da mai da hankali yayin da suke sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...

Sanata Barau zai baiwa dalibai 1,000 tallafin karatu a Kano ta tsakiya da ta Kudu

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau...

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...