Ramadan: Dan wasan kannywood Mustapha Naburaska ya fitar da Mutane 33 daga gidan yari

Date:

Daga Safiyya Adam Haske

 

Shahararran jarumin masana’antar Kanywood Mustapha Badamasi Naburaska ya biya tara ga akalla Mutane 33 Waɗanda suka daure a gidan gyaran hali na gwauron dutse dake nan kano.

Jarumin wanda kuma mataimakinw na musamman ga gwamnan Kano ya biya tarar Maza 31 da Mata 2 Waɗanda suka shaki iskar yanci Sakamakon kyautayin da Naburaska ya nuna musu.

Mustapha Naburaska yace ya gudanar da Wannan abun alkhairi ne sakamakon karatowar watan Azumin Ramadana, da kuma Neman yardar Allah da Neman lada a gare shi.

” Zaman gidan gyaran hali a irin wannan lokaci akwai matsi sosai ga dan adam, hakan tasa na biya tarar su don su fito su inganta Rayuwar su na nan gaba.” Inji Naburaska

Jarumin ya bukaci mawadata dake cikin al’ummar da su Gudanar da irin wannan aikin na fitar da al’umma Daga kangin rayuwa don su nemi lada a wajen Ubangiji Kuma su kyautata Rayuwar wasu.

Anasu bangaren wadanda suka shaki iskar yancin sun mika Sakon Godiyar su ga NaBraska da kuma Mutanen da suke irin wannan fitar da mutanen daga gidan gyaran halin.

A karshe dai mutanen sun lashi matakin za suy gyara halayen su bayan sun komawarsu Cikin ga iyalan su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...