IPMAN ta nemi afuwar al’umma bisa sayar musu da gurbataccen Man fetur

Date:

Daga Hamida Nasiru

Kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Najeriya IPMAN, ta nemi afuwar jama’a kan sayar da gurbataccen mai da mambobinta suka yi a fadin kasar.

Kadaura24 ta rawaito Shugaban kungiyar IPMAN reshen Kano, Alhaji Bashir Danmallam ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Kano ranar Talata.

Ya ce kungiyar ta ga ya dace ta nemi afuwar jama’a bayan da ta gano cewa man da ‘ya’yanta suka sayo daga Legas da Warri da sauran wurare gurbataccene Kuma an sayarwa al’umma shi.

“Mambobin mu sun sayi kayan ne daga Legas, Warri da sauran wuraren da aka ajiye ba tare da sanin gurbatattu bane.

“Don haka, mun ga ya dace mu nemi afuwar jama’a kan lamarin domin kada a zargi mambobinmu domin ba laifinsu ba ne,” in ji shugaban IPMAN.

Sai dai ya zargi jami’an gwamnati da ke aiki a dakunan gwaje-gwaje da rashin sanar da mambobinsu Cewa man gurbatattune.

A cewarsa, jami’an da ke aiki a dakunan gwaje-gwajen na da hurumin gano gurbatattun Mai tare da sanar da mambobinsu don kada su saya su sayar wa jama’a.

Dan Malam ya bayyana cewa kungiyar ta tuntubi Manajan Daraktan Kamfanin Tallan Kayayyakin Man Fetur (PPMC), Mista Isiyaku Abdullahi wanda tun a lokacin ya umarci duk ‘yan kasuwar da suka sayi gurbataccen samfurin da su mayar da shi inda suka saya.

Danmalam ya bada tabbacin cewa IPMAN za ta hada kai da mahukuntan kamfanin man fetur na kasa (NNPC) domin hana afkuwar afkuwar lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...