Yan sanda a kano sun kuɓutar da wani matashi da aka kusa yi wa yankan rago

Date:

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce ta kuɓutar da wani matashi da ake zargin wasu yan damfara sun yi yunƙurin yi wa yankan rago.

Lamarin ya faru ne a wani gida a ƙaramar hukumar Dambatta a Kano.

Kakakin rundunar ƴan sandan DSP Abdullahi Kiyawa ya shaida wa BBC cewa sun sami labarin faruwar lamarin ne bayan da matashin da aka fara yankawa makogoro ya kai musu ƙorafi.

Ya ce nan take suka garzaya da shi asibiti.

Matashin, mai shekara 23, ya bayyana wa BBC cewa a dandalin sada zumunta na Facebook suka haɗu da wanda ake zargi da yunƙurin halaka shi.

A makon da ya gabata ma an kama wani matashi da ya yi wa wata yarinya ‘yar makotansu yankan rago a karamar hukumar Tofa a Kano, bayan ya nemi kudin fansa daga wajen iyayenta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano Ta Karyata Rahoton Cibiyar Wale Soyinka Kan Take ‘Yancin ‘Yan Jarida

Gwamnatin Jihar Kano ta yi watsi da rahoton da...

Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Cire Maryam Sanda Daga Jerin Wadanda Za a Yi Wa Afuwa

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya bada umarnin a...

Majalisar Kano ta buƙaci a soke ɗaukar aikin kwastam da aka yi a kwanan nan

Majalisar dokokin jihar Kano ta yi kira ga dukkan...

‎ ‎Kuskure ne Tinubu ya cigaba da ciyo wa Nigeria bashi bayan ya cire tallafin mai – Sarki Sanusi

‎ ‎ ‎Sarkin Kano kuma tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN),...