Daga Rukayya Abdullahi Maida
Gwamnatin jihar kano ta bukaci jami’an tsaron dake kasar nan da su yi amfani da ranar ta tunawa da yan mazan jiya ta shekara 2022, wajen auna irin aiyukan da suke gudanarwa domin magance matsalolin tsaro da suka addabi kasar nan.
Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi umar Ganduje ne ya bayyana hakan lokacin da ya halaccin taron tunawa da tsafaffin sojojin Nigeria wadanda suka rasa rayukansu yayin yakin duniya na daya dana biyu dama yakin basasa.
Gwamnan yace idan akai la’akari da gudunmawar da tsafofaffin sojojin suka bayar akwai bukatar jami’an tsaron wannna lokaci su yi koyi da su wajen sadaukar da kai domin kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Nigeria.
Yace ya zama wajibi a rika yiwa tsofaffin sojojin addu’o’i saboda da rawar da suka taka wajen tabbatuwar Nigeria matsayin kasa daya dunkulalliya.
Ganduje ya kuma bada tabbacin gwamnatin jihar kano zata cigaba da tallafawa Kungiyar tsofaffin sojojin da kuma iyalan wadanda suka rasa rayukansu yayin kare martabar kasar nan .
Kadaura24 ta rawaito yayin taron dai an gudanar da addu’oi da fareti tare kuma da sanyan fure Wanda ke nuna tausayawa da kuma yabawa tsofaffin sojojin, taron dai ana gudanar da shi duk ranar 15 ga watan janairun ko wacce shekara.