Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta Soke Jarrabawa saboda Yajin Aikin ‘Yan adaidaita Sahu

Date:

Daga Maryam Muhd Zawaciki

Jami’ar Yusuf Maitama Sule to soke jarrabawar da za ta gudanar da karfe 8 zuwa 11 na safe a gobe Litinin biyo bayan shirin tafiya yajin aiki da matuka babun adaidaita sahu suka yi.

Kadaura24 ta rawaito wanna na kunshe cikin wata sanarwar da shugaba kwamitin shirya jarrabawar Jami’ar Dr Yau Datti ya fitar ranar Lahadin nan.

Sanarwar ta ce kwamitin zai tuntubi shugaban Jami’ar domin yanke hukunci kan makomar sauran jarrabawar da za a rubuta.

Tun kwanaki uku da suka wuce yan Sahun suka raba takardun Kira ga matukan da su shiga yajin aikin mako guda don nuna adawarsu ga sabunta koriyar lamba da hukumar KAROTA ta ce suyi.

Haka kuma tun da yammacin yau Lahadi aka ga sun fara sanya ganye alamar yajin aikin na man daram babu gudu babu ja da baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...

Ra’ayi:‎Tsarin Kwankwasiyya ya dora Kano a gwadaben cigaba a mulkin Gwamna Abba Kabir -Adamu Shehu Bello

‎ ‎Ra’ayi ‎ ‎Daga Adamu Shehu Bello (Bayero Chedi), Jigo a Kwankwasiyya...

Al’ummar Garin Riruwai da wani Kamfanin Hakar ma’adanai Sun Cimma Yarjejeniya Kan Ci gaban yankin

Kwamitin ci gaban Al’ummar garajn Riruwai da wani kamfanin...