Shirya taron zumunci zai wanzar da zaman lafiya a ƙasa – Ɗan kadan Kano

Date:

Daga. Nasiba Rabi’u Yusuf
Ɗan kadan Kano kuma Dan majen Gwandu Alhaji Bashir Ibrahim  Muhammad ya buƙaci al’umma da su riƙi zumunci a matsayin abinda zai ƙara kyautata alaƙarsu da yan uwan su a duk inda suke.
KADAURA24 ta rawaito Alhaji Bashir Ibrahim ya bayyana hakan a ranar Litinin, a wajen taron zuriyar Marigayi Moddibo Mahmud da kuma gabatar da littafin tarihin zuri’ar.
Ɗan kadan Kanon ya ce, kowacce zuri’a tana yin ƙarko ne a duk sanda ƴaƴan cikinta suka ɗauki matakan ingantata musamman ta hanyar shirya taruka.
“Muna sane da tarihin yadda kowacce zuriya ke fara da kaɗan, sai kuma ta bazu zuwa sassan duniya ta ci gaba da yaɗuwa ta hanyar hayayyafa”.
Zuri’ar Moddibo ta zo Kano ne tun daga zamanin marigayi sarki Abdullahi Maje Karofi ga shi a yanzu zuriyar ta fara tattaro kanta ta hanyar bincike da tuntuɓa”.
Alhaji Bashir Ibrahim ya kuma ce, ta hanyar shirya taron dangi ne za a san yawan zuri’a kuma zumunci zai ƙara danko da kuma samu haɗin kani da zaman lafiya.
Taron ya samu halartar ɗaukacin ƴaƴa da jikoki daga sassa daban daban na ƙasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta magantu kan Hukuncin kotu na zaben kananan hukumomi

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Kano ta bayyana farin...

Kotun daukaka kara ta yanke hukunci kan zaben kananan hukumomin Kano

Kotun ɗaukaka kara dake Abuja, ta rushe hukuncin babbar...

Dole ne yan Nigeria su dage da yawaita addu’o’i a kwanaki 10 Zulhijja – Sheikh Muhd Nasir

Daga Usman Hamza Shugaban majalisar limaman masallatan juma'a na Nigeria...

Mun kama mutanen da mu ke zargi da kashe DPO Rano – Kiyawa

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta...