Shirya taron zumunci zai wanzar da zaman lafiya a ƙasa – Ɗan kadan Kano

Date:

Daga. Nasiba Rabi’u Yusuf
Ɗan kadan Kano kuma Dan majen Gwandu Alhaji Bashir Ibrahim  Muhammad ya buƙaci al’umma da su riƙi zumunci a matsayin abinda zai ƙara kyautata alaƙarsu da yan uwan su a duk inda suke.
KADAURA24 ta rawaito Alhaji Bashir Ibrahim ya bayyana hakan a ranar Litinin, a wajen taron zuriyar Marigayi Moddibo Mahmud da kuma gabatar da littafin tarihin zuri’ar.
Ɗan kadan Kanon ya ce, kowacce zuri’a tana yin ƙarko ne a duk sanda ƴaƴan cikinta suka ɗauki matakan ingantata musamman ta hanyar shirya taruka.
“Muna sane da tarihin yadda kowacce zuriya ke fara da kaɗan, sai kuma ta bazu zuwa sassan duniya ta ci gaba da yaɗuwa ta hanyar hayayyafa”.
Zuri’ar Moddibo ta zo Kano ne tun daga zamanin marigayi sarki Abdullahi Maje Karofi ga shi a yanzu zuriyar ta fara tattaro kanta ta hanyar bincike da tuntuɓa”.
Alhaji Bashir Ibrahim ya kuma ce, ta hanyar shirya taron dangi ne za a san yawan zuri’a kuma zumunci zai ƙara danko da kuma samu haɗin kani da zaman lafiya.
Taron ya samu halartar ɗaukacin ƴaƴa da jikoki daga sassa daban daban na ƙasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NAHCON ta sanar da ranar da za a fara jigilar Maniyatan Nigeria zuwa kasar Saudiyya

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar kula da aikin hajji ta...

Hisbah ta rushe wajen da aka ce sawun Ma’aiki ya fito a jihar Kano

    Hukumar Hisbah ta kai samame tare da rushe wani...

ƴan siyasa ne su ka kashe Arewacin Nigeria — Inji Gwamna Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa ‘yan...

Shugaban Karamar hukumar Bagwai ya kaddamar da aikn gada ta sama da Naira Miliyan 160

Daga Shu'aibu Sani Bagwai   Karamar hukumar Bagwai a jihar Kano...