Luguden wuta ya Tilastawa Bello Turji Neman Sulhu da Gwamnatin Tarayya

Date:

Kasurgumin dan bindigar da ya addabi jama’ar yankin arewa maso yammacin kasar nan Bello Turji, ya nemi yin sulhu da gwamnati, sakamakon barin wutar da dakarun. sojojin kasar ke cigaba da yi musu a dazukan da suke boye.

Wata majiya ta ce Turji ya nemi yin sulhu gami da alkawarin ajiye makamansa ne, cikin wata wasika da ya aike da nufin isar da it aga gwamnan Zamfara Bello Matawalle da kuma shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
Cikin labarin da ta wallafa a shafinta na yanar gizo, Jaridar Daily Trust da ke Najeriya ta ce wani mazaunin yankin Shinkafi a jihar Zamfara ya tabbatar mata da gaskiyar labarin.
Tun daga ranar Alhamis 16 ga watan Disamba, dakarun Najeriya ke yi wa ‘yan bindiga luguden wuta a kauyen Katanga da ke jihar Sokoto a karamar hukumar Isa.
Wadanda suka shaida lamarin sun ce babban kwamandan sojin dake kula da runduna ta 8 Manjo Janar Uwem Bassey ne ke jagorantar tawagar sojoji tare da manyan jami’an sa a cikin motocin yaki sama da 20, wadanda suka yi wa ‘yan bindigar kofar rago, yayin da sojin sama ke taimaka musu da ruwan wuta ta sama.
Jihar Sokoto na daya daga cikin Jihohin Arewa maso Yammacin Najeriya da ‘yan bindiga suka mamaye wasu sassanta, inda suke kai munanan hare hare suna kashe mutane.
Makwanni biyu da suka gabata, ‘yan bindigar suka kai kazamin hari karamar hukumar Sabon Birni inda suka kona wasu matafiya sama da 40 a cikin motar su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...

An sake sauya lokacin jana’izzar Aminu Ɗantata – Gwamnatin Nigeria

Gwamnatin tarayyar Nigeria ta ce Hukumomi a Kasar Saudiyyar...

Fadan daba: ku fito ku Kare Kan ku da iyayenku – Gwamnatin Kano ga matasa

Ku tashi ku Kare kanku da iyayen Gwamnatin jihar kano...