Sheikh Kabiru Gombe ya bayyana Dalilan da suka sa basa Kalubalentar Buhari a Mubarinsu

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Sannanne Malamin addinin Musulcin nan a Nigeria Sheikh Kabiru Haruna Gombe ya ce basa Kalubalentar Buhari ne a Mubarinsu Saboda Yana basu damar su je Wajen suyi Masa Nasiha.

Cikin wani video Malamin yace Wani Dan Siyasa ya tambaye shi Dalilin da yasa suke yiwa Buhari uziri Kuma Suka ki yiwa tsaron Shugaban kasa Goodluck Jonathan uzirin.

KADAURA24 ta rawaito Sheikh Kabiru Gombe yace ya baiwa Mai tambayar amsa da Cewa shi Shugaban kasa Buhari yana kiransu Lokaci Bayan Lokaci don su yi masa nasiha kuma su bashi shawara ,yace amma tsohon Shugaban kasa Jonathan baya basu irin Wannan dama kawai Yana bada damar ne ga Malaman addinin su.

 

Rashin tsaron:Buhari ya tura Shugabanin Hukumomin tsaro jihohin Katsina da Sokoto

Yace akwai abubu da dama wanda Buhari ya yi su ne sakamakon nasihar da sukai Masa da Kuma shawarwarin da suka bashi.

Idan Shugaba zai baka dama kaje kusa dashi kayi masa nasiha to haramun ne ka kalubalance shi a Kan Mubarin” inji Sheikh Kabiru Gombe

A Wannan lokaci dai al’umma Su na ta kokawa Kan kin yin magana ga Malamai akan abubuwan da suke faruwa na rashin tsaro a Arewacin Nigeria, Amma Kuma a gwamnatin baya ta Goodluck Jonathan an Sha Jin Malamin da wasu malaman Suna kalubalantar salon jagorancin sa musamman Kan aiyukan yan Boko Haram.

2 COMMENTS

  1. קמגרה תשדרג לכם את חיי המין ותאפשר לכם הנאה מרבית מהאקט. לטבע פלז’ר שלל פתרונות טבעיים נוספים שישדרגו לכם את חדר המיטות. קמגרה תשדרג לכם את חיי המין ותאפשר לכם הנאה מרבית מהאקט. לטבע פלז’ר שלל פתרונות טבעיים נוספים שישדרגו לכם את חדר המיטות. מכוני ליווי

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta fara biyan tsofaffin kansilolin APC hakkokinsu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir...

Abun da ya faru a Rano ba sai sake faruwa – Shugaban karamar hukumar ya tabbatar

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Shugaban karamar hukumar Rano malam muhd...

Bayan ganin wata Zulhijja, Saudiyya ta sanar da Ranar Arfat

Hukumomi a kasar saudiyya sun tabbatar da ganin jinjirin...

Kotu ta yanke hukuncin kisa ga matashin da ya kona masallata a Kano

Babbar Kotun Shari’a da ke Kano ta yanke hukuncin...