Duk da umarnin kotu, APC ta bayyana Bangaren Shekarau a matsayin haramtacce

Date:

Daga Zara Jamil Isa
  Shugabancin jam’iyyar APC ta kasa ya bayyana wani bangare na jam’iyyar a jihar Kano karkashin jagorancin Sanata Ibrahim Shekarau a matsayin haramtacce.
 Sakataren Kwamitin Tsare Tsare-Tsare na Jam’iyyar APC mai rikon kwarya, Sanata John James Akpanudoedehe, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a, babban birnin Abuja.
 Idan Zaku iya tunawa Kadaura24 ta rawaito wata babbar kotun Abuja ta amince da taron da bangaren Shekarau ya gudanar tare da soke na bangaren Gwamna Abdullahi Ganduje.
 Alkalin kotun, Mai shari’a Hamza Muazu, a hukuncin da ya yanke ya hana bangaren Ganduje aina kansu a Matsayin Shugabanin jam’iyyar a Jihar Kano .
 Bangaren Ganduje ya zabi Abdullahi Abbas a matsayin shugaban kungiyar, yayin da bangaren Shekarau ya zabi Haruna Ahmadu Danzago, a lokaci da aka gudanar a Zaben a  ranar 16 ga watan Oktoba.
 Da yake magana da manema labarai, Akpanudoedehe ya bayyana cewa zaben da bangaren Ganduje ya gudanar shi shugabannin jam’iyyar suka amince da su kuma shi ne akan ka’ida.
 Politics Digest ta rawaito John ya tabbatar da cewa jam’iyyar ba ta aika kwamitoci biyu don yin zabe kala biyua a jihar kano ba, yana mai bayyana mambobin da suka halarci taron da bangaren Shekarau ya gudanar a matsayin masu zagon kasa ga jam’iyyar.
 Sakataren jam’iyyar APC, ya bayyana cewa jam’iyya mai mulki ba ta samu ta yi nazarin hukuncin da kotu l ta tabbatar da bangaren Shekarau ba.
 “Mu ne shugabannin jam’iyyar Kuma mu mu ke da alhaki ba za mu so yin tsokaci kan hukuncin da ba mu gani ba.
 “Abin da zan iya gaya muku a yanzu shi ne, za mu nemi kwafin  hukuncin domin yin nazari akan sa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...