Shugaba Buhari zai tsaida ranar babban taron jam’iyyar APC

Date:

Daga Jidda Abubakar
 Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai yanke hukunci Dangane da Ranar da jam’iyya mai mulki ta APC ta Kasa zata gudanar da Babban taron jam’iyyar ta kasa.
 Shugaban kungiyar gwamnonin jam’iyyar APC, Gwamna Atiku Bagudu na jihar Kebbi ya shaida wa manema labarai hakanda bayan kammala taron gwamnonin, Inda yace za su nemi ganawa da shugaban kasa domin Sanya ranar da ta dace.
 Ana kyautata zaton cewa Gwamnonin za su kuma nemi goyon bayan Shugaban kasa kan yadda ake ta cece-kuce a kan batun Zaben fidda gwani na kato bayan Kato a cikin jam’iyyun siyasar Kasar nan tsakanin ‘yan majalisar dokokin Najeriya da jam’iyyun siyasa ciki har da babbar jam’iyyar adawa ta PDP.
 Haka kuma Gwamnonin sun bayyana ji dadinsu Kan yadda zaben Gwamnan Anambra ya gudana cikin kwanciyar hankali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zaizayar kasa: Gwamna Abba gida-gida ya raba diyyar Naira Miliyan 600 A Kano

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Dalilin da ya hana Sarki Aminu Ado Bayero zuwa gidan yari na goron dutse a yau alhamis

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Rahotanni sun tabbatar da cewa Sarkin...

Matakai 3 da gwamnatin Kano ta dauka kan kafafen yada labarai a jihar

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnatin jihar Kano ta ce a...

Yadda manoma a Kano suka zargi jami’an Civil defense da karbar kudade a wajensu

Daga Umar Ibrahim kyarana   Manoman dajin dansoshiya dake karamar hukumar...