Shugaba Buhari zai tsaida ranar babban taron jam’iyyar APC

Date:

Daga Jidda Abubakar
 Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai yanke hukunci Dangane da Ranar da jam’iyya mai mulki ta APC ta Kasa zata gudanar da Babban taron jam’iyyar ta kasa.
 Shugaban kungiyar gwamnonin jam’iyyar APC, Gwamna Atiku Bagudu na jihar Kebbi ya shaida wa manema labarai hakanda bayan kammala taron gwamnonin, Inda yace za su nemi ganawa da shugaban kasa domin Sanya ranar da ta dace.
 Ana kyautata zaton cewa Gwamnonin za su kuma nemi goyon bayan Shugaban kasa kan yadda ake ta cece-kuce a kan batun Zaben fidda gwani na kato bayan Kato a cikin jam’iyyun siyasar Kasar nan tsakanin ‘yan majalisar dokokin Najeriya da jam’iyyun siyasa ciki har da babbar jam’iyyar adawa ta PDP.
 Haka kuma Gwamnonin sun bayyana ji dadinsu Kan yadda zaben Gwamnan Anambra ya gudana cikin kwanciyar hankali.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...